Mama tashiga nan nan da diyarta kanneta zagaye daita kowannesu Na murna ganinta hatta aunty Salma tazo da murnata wace ummi ce tasanar mata da zuwan Nablah din . gabadayansu ,suka saka nablah a tsakiyar su .suna murna da jin dadi ganinta .
nuratu ta kalli nablah da kyau .
Kai Alhamdulilllahi yau dai zamu huta da shan zagi gurin baba.
Na aunty Salma ta tsiyar masa da "ya" nablah tayi murmushi wanda ke karawa fuskarta kyau da annuri tare da cewa banana kennan.
nayi kewarsa nima sosai fiyye da tunaninku ..uhm kalli yadda kika dawo Nablah kinyi kyau dake kikayi fresh sosai gadabaya fatar jikinki ta sauya wlh gurin nan ya amsheki inji cewar nuratu ..
Allah ko nablah tace hk tana murmushi sannan tacigaba duk wannan kyawun da fresh din danayi wlh nafi son gidanmu koda kuwa za'a kwana bamu ci ba Amman dai zan koma sbd wani dalili nawa .. aunty Salma tayi saurin cewa wlh bada hannuna ba 'cikin komawarki .
Ni dai tunda kin dawo Na auna arziki Na huta da fadan baba wlh har fargaba zuwa gidan nan nake .
Tun tafiyarki nake 'cikin tashin hankali boye miki kawai nakeyi sbd kwanciyar naki hankalin Amman mgnr gsky Na tsorata da al'amarin baba.. nan nuratu tashiga zaiyanewa nablah labarin duk abinda ya faru da yadda aunty Salma ke shiri idan zatazo gida .
aiko gabadayansu suka kwashe da wata mahaukaciyar dariya .Maman da tun sanda suka fara hirasu da nuratu da Salma ba tsoma musu baki ba sai yanzu tace uhmmmm nablah bana jin babanki zai yarda ki sake barin gidan nan ballanantana har ki koma wani aiki.
ni kaina wlh yanzu banaso komarwaki .
dan hk bbu inda zaki ki zauna kema 'cikin yan'uwanki zan fi samun kwanciyar hankali .
Aunty Salmah tace wlh zanceki gaskiya ne mama Amman kubari baban yazo tukun nasan da zarar yasanar mata da abinda ya zartar akanta zata natsu ... ko babu wannan dalilin bazata koma koina ba inji cewar mama .
murmushi takaici nablah tayi tare da cewa Mama kennan Allah Ni dai zan koma wlh Amman Na da wata uku zan dawo gabadaya gareku.
mama dan Allah kada kice a'a ta karasa mgnr tana marairaice muryar .
uhmmmm mama ta sauke ajiyar zuciya to shikennan Amman kibari babanki yazo kiji me zaice.
Take sukar bar zance suka shiga wata hirar daban .
karfe hudu daidai sai Ga direban ummi ya dawo daukar nablah Amman nablah ta fita da kanta tace ba yau zata koma ba sai zuwa jibi ko gata. da zai wuce aunty Salma ta bishi Dan ya rage mata hanya .Da daddare byn sallar isha'i mlm salisu yashigo gidan da sallama a bakinsa hannushi rike da wata bakar leda yana shiga dogon parlour gidan.
idanunshi suka sauka kan diyarsa nablah dake sanye da hijab ajikinta wanda tun safe datazo gidan bataci re ba tana kwakume dashi abinda Yasa ma mama bata mata maganar ta cire ba sbd tasan tun asali hk take mayar hijabi ce ita ko bacci zatayi bata cirewa ..Ahankali mlm salisu yakarasa shigowa ciki tare da cewa wanake ganin hk kmr nablah agidan nan ?
Nuratu ta tashi da sauri jikinta a sanyaye ta karbi ledar hannushi ta ajiye a gefe tana mishi sannu da zuwa .
Bai kulata ba sbd hankalinsa dake kan nablah ..tsam itama nablah tayi da ranta tare da shan jinin jikinta sbd ganin irin kallon da mahaifin nata ke jifanta dashi .
jikinta a matukar sanyaye ta bude bakinta da kyar gurin cewa sannu da zuwa baba ..uhmmmm yauwa Yan neman abun duniya da fatan dai kin samo masu yawa ?
Nablah tayi tsit ta sake sha jinin jikinta ai nasan duk inda kika je zaki dawo , indai nine ubanki ba shegiya bace ke.....
yakarasa mgnr yana nunata da yatsa hannushi haba haba baban Salma tun...ke ...nasakaki cikin maganata ? Ya katse mama Yacigaba da mgnrsa .
Da "yata" nabeelah nake mgn ba da saratu ba .
dan hk banason jin bakinki cikin manta .
,ai duk da hadin bakinki yaran nan suke yi duk isakanci da sukaga dama.
basu dauke ni abakin komai ba km wlh duk lalacewata ni nan nine ubansu dole km akirasu da sunana sai dai mutun ya gudu bazan fasa mgn ba da cin uwar yarinya tsit kake jin gurin tamkar babu wasu halittu acikin parlour ..mlm salisu yacigaba har ni ubanki zance miki banason abu kice sai kinyi dole .

YOU ARE READING
AUREN SIRRI COMPLETE
Mystery / ThrillerMatar shi ce ta farko bata san haihuwa, idan ta samu ciki sai ta zubar, as ending yake yin auren sirri da mai aikin gidan